HomeLabaraiTa Shaƙi Iskar 'Yanci Bayan Shafe Shekara Tara A Hannun 'Yan Ta’adda...

Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Shekara Tara A Hannun ‘Yan Ta’adda A Borno

Daga Ishaq S. Hamza 

Dakarun sojin Najeriya sun ceto wata mata mai shekaru 25, Rukaya Mohammed, tare da ‘ya’yanta biyu, bayan da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da ita a shekarar 2017 a Jihar Borno.

Jaridar TheCable ta rawaito cewa, an ceto Rukaya da ‘ya’yanta, Hauwa Mustapha mai shekaru shida da Fati Mustapha mai shekaru huɗu, a yayin wani samame da sojoji suka kai a kusa da gadar Amuda a ranar 14 ga Agusta, 2026.

ƘARIN LABARI:

NSCDC Ta Damƙe Ɓarayin Babura A Nasarawa 

Rahotanni sun ce Rukaya ta shaida wa sojojin cewa tun a 2017 aka sace ta sannan aka tilasta mata yin aure da wani ɗan ta’adda, inda ta zauna a Wunje.

Ta samu damar tserewa ne bayan wasu daga cikin ‘yan ta’addan suka bar sansanin sakamakon rikicin da ya ɓarke a tsakaninsu.

Dakarun sun mika Rukaya da ‘ya’yanta ga hukumomin da abin ya shafa domin ɗaukar matakan da suka dace.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments